Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, an bude wasu ajujuwan wucin gadi na koyar da karatun kur’ani mai tsarki ga kananan yara a birnin Harare fadar mulkin kasar Zimbabwe.
Karamin ofishin jakadancin kasa Iran a kasar Zimbabwe ne ya dauki nauyin wanann shiri, domin yada koyarwar kur’ani mai tsarkia tsakanin musulmin kasar marassa rinjaye, wanda kuma shirin ya samu karbuwa daga musulmin kasar.
Baya ga haka kuma akwai wasu shirye-shiryen na asar kur’ani, wanda ake bayar da kyautuka na musamman ga wadanda suka nuna wazo.