Tashar talabijin ta UNB ta bayar da rahoton cewa, a cikin wata wasika da ta aike wa shugaban Falastinawa Mahmud Abbas, Firayi ministar kasar Bangaladesh Sheikh Husaina ta bayyana matsayin kasarta dangane da cin zalun da Isra'ila take a kan al'ummar Falastinu.
Ta ce abin da yake faruwa na kai hare-haren da Isra'ila take yi a kan al'ummar Falastinu abin yin tir da Allawadai ne.
Haka nan kuma ta jaddada cewa a kowane lokaci kasar Bangaladesh da al'ummarta za su ci gaba da kasancewa tare da al'ummar Falastinu.
Sannan ta kirayi kasashen duniya da su sauke nauyin da ya rataya a kansu an ganin sun taka wa Isra'ila burki dangane da kisan kiyashin da take kan al'ummar Falastinu.
Baya ga haka kuma ta yi kira da a gaggauta samar da hanya wadda za ta baiwa falastinawa damar kafa kasarsu mai cin gishin kanta.