Shafin yda labarai na Bawwaba ya bayar da rahoton cewa, cibiyar Azhar ta kasar Masar ta girmama Ru'a Muhammad ahmad wata yarinya da ta rubuta cikakken kwafin kur'ani mai tsarki.
Sheikh Mumin Alhawari shi ne shugaban reshen cibiyar azhar a yankin Bahrul Ahmar, ya kuma halrci makarantar sakandare da Ru'a take karatu, inda a nan ne aka gabatar da da wannan kwafin kur'ani da ta rubuta da hannunta.
A madadin cibiyar ta Azhar shehin malamin tare da tawagarsa da suka halarci wurin sun mika kyautuka na musamman ga wannan yarinya amatsatin girmamawa da jinjina agare ta kan wannan babban aiki da ta yi.