IQNA

Azhar Ta Girmama Wata Yarinya Da Ta Rubuta Kur'ani A Masar

23:48 - May 23, 2021
Lambar Labari: 3485941
Tehran (IQNA) cibiyar Azhar ta girmama wata yarinya da ta rubuta cikakken kwafin kur'ani mai tsarki a Masar.

Shafin yda labarai na Bawwaba ya bayar da rahoton cewa, cibiyar Azhar ta kasar Masar ta girmama Ru'a Muhammad ahmad wata yarinya da ta rubuta cikakken kwafin kur'ani mai tsarki.

Sheikh Mumin Alhawari shi ne shugaban reshen cibiyar azhar a yankin Bahrul Ahmar, ya kuma halrci makarantar sakandare da Ru'a take karatu, inda a nan ne aka gabatar da da wannan  kwafin kur'ani da ta rubuta da hannunta.

A madadin cibiyar ta Azhar shehin malamin tare da tawagarsa da suka halarci wurin sun mika kyautuka na musamman ga wannan yarinya  amatsatin girmamawa da jinjina  agare ta kan wannan babban aiki da ta yi.

تجلیل از دانش‌آموز مصری که کل قرآن را کتابت کرده است + عکس
 
تجلیل از دانش‌آموز مصری که کل قرآن را کتابت کرده است + عکس
 
تجلیل از دانش‌آموز مصری که کل قرآن را کتابت کرده است + عکس
 
تجلیل از دانش‌آموز مصری که کل قرآن را کتابت کرده است + عکس
 
تجلیل از دانش‌آموز مصری که کل قرآن را کتابت کرده است + عکس

 

3973149

 

 

captcha