A jajibirin aiwatar da hukuncin "Alkawari na Gaskiya" kan gwamnatin sahyoniya, Jagoran juyin juya halin Musulunci a daya daga cikin tarurrukan da suka danganci hakan ya rubuta wata aya daga cikin wakokin da ya rubuta a 'yan shekarun da suka gabata tare da ishara daga ayoyin Alkur'ani mai girma game da arangamar da Annabi Musa (A.S) ya yi da Fir'auna da matsafan Fir'auna. A kan haka ne kuma ta hanyar daidaita hoton makamai masu linzami na Iran da jirage marasa matuka da ke wucewa ta kan majalisar Knesset (Majalisar dokokin Sahayoniya) a lokacin farmakin Alkawarin Gaskiya , ya fitar da rubutu mai taken "Jefa sanda".
18:38 , 2024 May 05