IQNA

An Kafa Wata Kungiya Agaji A Najeriya Da Ta Hada Musulmi Da Kiristoci

14:54 - September 09, 2016
Lambar Labari: 3480769
Bangaren kasa da kasa, an kafa wata kungiyar bayar da agaji a tarayyar Najeriya wadda za ta rika taimakawa a bangarori rayuwar jama’a.
Kamfanin dillancin labaran kur’ani na iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na jaridar Vanguard cewa, a jahar Borno da ke Najeriya an kafa wata kungiyar bayar da agaji wadda za ta rika taimakawa a bangarori rayuwar jama’a, da hakan ya hada da tsaftace masallata d akuma majami’oi, inda yanzu haka kimanin mutane dari ne suka yi cikakkiyar rijistar zama mambobi na kunfiyar.

Auguns Bashir daya ne daga cikin shugabannin kungiyar ya bayyana cewa, babbar manufarsu ita ce yada sulhu da fahimtar juna da zaman lafiya a tsakanin dukkanin al’ummar Najeriya baki daya, wadda ta hada mabiya addinai daban-daban musamman ma dai musulunci da kiristanci.

A halin azu dai jahar Borno ita ce jaha ta farko da kungiyar ta fara aiwatar da shirinta, kuma zai ci gaba da gudana zuwa sauran jahohi a lokuta masu zuwa.

Tun a cikin shekara ta 2002 ne dai Muhammad Yusuf ya kafa kungiya wadda ke dauke da akidar wahabiyanci wadda ta rikide ta koma Boko Haram daga bisani, wadda ke kaddamar da hare-haren ta’addanci tare da kashe fararen hula da jami’an tsaro.

3528604


Abubuwan Da Ya Shafa: iqna agaji najeriya borno boko haram
captcha