IQNA

An Rufe Makarantun Kur'ani A Kuwait Saboda Cutar Corona

23:53 - February 27, 2020
Lambar Labari: 3484566
Tehran - (IQNA) an rufe makamarantun kur'ani a kasar Kuwait saboda tsoron bullar cutar corona kamar dai yadda ma'aikatar kula da harkokin addini ta sanar.

Ma'aikatar kula da harkokin addini ta kasar Kuwait ta sanar ad rufe dukkanin makarantun kur'ani da cibiyoyin bincike na addini na addini  a fadin kasar, domin kaucewa kamuwa da cutar corona.

Wannan mataki ya zo bayan tattaunawar da ta gudana tsakanin ma'aikatun kula da harkokin addini da kuma ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar.

Tun bayan bayyanar cutar corona a kasar, Kuwait ta bayar da hotu a dukkanin makarantun boko da suka hada da firamare da sakandare da kuma jami'oin kasar.

Wadanda kuma ake zargin cewa suna dauke da cutar an killace ana kula da sua  wasu asibitoci na musamman.

 

3881853

 

 

captcha